Babban Sufeton ‘yan sandan Najeriya ya magantu kan kai wa jami’ansa hari
Babban sufeton ‘yan sandan Najeriya ya bayyana takaici kan yadda ya ce ana samun ƙaruwar hare-haren da ake kai wa ‘yan sanda a sassan ƙasar.
Babban sufeton ‘yan sandan Najeriya ya bayyana takaici kan yadda ya ce ana samun ƙaruwar hare-haren da ake kai wa ‘yan sanda a sassan ƙasar.
Yanzu haka ana fargabar cewa mutane 11,587 sun kamu da cutar mashako yayin da aka tabbatar da mutane 7,202 a kananan hukumomi 105 daga jihohi 18 da ke fadin kasar sun kamu da cutar, inda cutar ta yi sanadiyyar mutuwar mutum 453 a Najeriya. Kashi 73 cikin dari na wadanda suka kamu da cutar yara ne yan shekara 1 zuwa 14.
Daya daga cikin manyan kungiyoyin man fetur da iskar gas a Najeriya za ta shiga yajin aikin da za a fara daga ranar 3 ga watan Oktoba a fadin kasar domin nuna adawa da manufofin gwamnati da ke janyo wa ‘yan Najeriya kuncin rayuwa da tabarbarewar tattalin arziki, in ji shugabannin kungiyoyin.
Rahotanni daga garin Kwantagora a jihar Neja na nuna cewa wani kwalele-kwale ya nutse a cikin ruwa wanda ya yi sanadiyar rasuwar yayan fitaccen mawakin yabon Annabi SAW, Marigayi Sharif Rabi’u Usman Baba.Wani dan uwan mamatan Malam Usman Tijjani Baba, ne ya bayyana haka a cikin tattaunawarsa da gidan radiyon Freedom a jiya.
Hukumar Raya Birnin Abuja ta bayyana cewa za ta fara kamen fasinjojin dake hawa achaba. Hukumar wadda ke karkashin jagorancin ministan Abuja, Nyesom Wike ta ce idan ta kama fasinjoji masu hawa achaba dole a bar yin sana’ar a birnin.
Gwamnatin Mulkin Soji ta ƙasar Burkina Faso ta sanar da cewa ta yi nasarar daƙile wani yunƙurin juyin mulki da aka yi a ranar Talata.
Hukumar bunƙasa harkar noma ta jihar Kano (KSADP), za ta kashe kimanin Naira miliyan 600 domin gudanar da ayyukan inganta kasuwar hatsi ta kasa da kasa da ke Dawanau.
Ministan Harkokin Cikin Gida, Dr. Olubunmi Tunji-Ojo, ya ayyana Litinin 2 ga watan Oktoba a matsayin hutu a faɗin ƙasar nan domin tunawa da cikar Najeriya shekaru 63 da samun ‘Yancin Kai.
Kamar yadda hukumar lafiya ta duniya Ke bayyana irin barazanar da mata da kananan yara ke fuskanta na karancin abinci mai gina jiki a nahiyar afirka.
Za mu kawo karshen cire wa mutane kudi da bankuna ke yi ~ CBN