‘Ya’yan Fitaccen Mawaki, Rabi’u Usman Baba, Sun Rasu

Rahotanni daga garin Kwantagora a jihar Neja na nuna cewa wani kwalele-kwale ya nutse a cikin ruwa wanda ya yi sanadiyar rasuwar yayan fitaccen mawakin yabon Annabi SAW, Marigayi Sharif Rabi’u Usman Baba.Wani dan uwan mamatan Malam Usman Tijjani Baba, ne ya bayyana haka a cikin tattaunawarsa da gidan radiyon Freedom a jiya.

Usman ya ce hadarin ya faru ne da safiyar yau Alhamis a kan hanyarsu ta zuwa wani gari a cikin Kwantagora don halartar bikin Mauludi kamar yadda su ka saba a kowacce shekara.

Ya kara da cewa, bayan samun nasarar fitowa da mutane shida da jirgin ya nutse da su cikin ruwan, an garzaya da su asibiti in da a nan ne aka tabbatar da rasuwar mutum biyu daga cikinsu.Wadanda su ka rasun su ne Khalifa Sharif Fatuhu Rabi’u Usman Baba da dan uwansa Nafsuzzakiya Rabi’u Usaman Baba.

Kamar yadda dan uwan mamatan ya tabbatar an dauko gawarwakin zuwa Kano domin yi jana’izarsu a yau Juma’a da misalin karfe 2 na rana a masallacin Juma’a na Sheikh Isyaka Rabi’u da ke unguwar Gwauron dutse cikin birnin Kano.

Post masu alaƙa

Da Fulani Aka Kama da Wuraren ƙera Makamai a Filato, da War Haka Duniya ta Dauka:-Zagazola Makama

Gwamna Bala Mohammed ya canja sheka daga jam’iyar PDP zuwa jam’iyyar APM

Gwamnatin Jihar Jigawa ta raba rancen naira miliyan dubu huɗu