Zan tabbatar matatun man Najeriya sun koma aiki – Tinubu
Shugaban Najeriya, Bola Ahmed Tinubu ya ce zai farfaɗo tare da tabbatar da cewa matatun man ƙasar, da suka jima ba sa aiki, za su koma aiki. Shugaban Tinubu ya bayar da tabbacin ne a ranar Alhamis, lokacin da Ƙungiyar Ma’aikatan Man Fetur da Iskar Gas ta Najeriya (NUPENG) suka kai masa ziyara a fadarsa. […]