Dokta Hakeem Baba Ahmed Ya Ajjiye Mukamin Da Gwamnatin Tinubu Ta Bashi
Tsohon mai magana da yawun kungiyar Dattawan Arewacin Najeriya Dokta Hakeem Baba-Ahmed, ya yi murabus daga matsayin mai bai wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin siyasa.
Tsohon mai magana da yawun kungiyar Dattawan Arewacin Najeriya Dokta Hakeem Baba-Ahmed, ya yi murabus daga matsayin mai bai wa Shugaba Bola Tinubu shawara kan harkokin siyasa.
Asusun Bada Lamuni na Duniya (IMF), ya buƙaci Gwamnatin Najeriya ƙarƙashin jagorancin shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da cewa manufofin tattalin arziƙin ƙasar sun kare muradun mutane masu ƙaramin ƙarfi.
Shugaban ƙasar Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya yi Allah-wadai da kisan mutane 16 da aka yi a jihar Edo, yana mai umartar hukumomin tsaro da su kamo waɗanda suka yi wannan mummunar aika-aikar.
Tsohon gwamnan jihar kano kuma shugaban Jam’iyyar APC na Ƙasa, Dr Abdullahi Umar Ganduje, ya ce babu wata gamayyar ’yan adawa da za ta iya hana Shugaba Bola Ahmed Tinubu lashe wa’adi na biyu a zaɓen 2027 idan Allah ya kai mu.
Majalisar Wakilan Najeriya ta amince da dokar ta baci, da kuma dakatarwar da shugaba Tinubu ya yi wa gwamanan jihar Ribas Siminalayi Fubara cikin yanayi na kusan na bai daya.
A ranar Talata ne, Shugaba Tinubu ya sanar da sanya dokar ta-ɓaci a Jihar Ribas, inda ya bayyana cewa rikicin siyasar jihar yana barazana ga zaman lafiya da tsaron al’umma.
Wannan mataki ya janyo ce-ce-ku-ce a faɗin Najeriya, inda mutane da dama ke ganin hakan bai dace da kundin tsarin mulki ba.
Ƙungiyoyin NLC da TUC sun buƙaci Shugaba Tinubu da ya gaggauta janye wannan mataki, don kada ya jefa Najeriya yanayin saɓa wa doka a nan gaba.
Shugaban kasa Bola Ahmed Tinubu ya ba da umarnin kammala aikin babbar hanyar Abuja zuwa Kano cikin wata 12 masu zuwa kamar Yadda Mai magana da yawun fadar shugaban Sunday Dare, ya sanar.
Gwamnatin Najeriya ta jinjinawa rukunin kamfanin Dangote saboda da muhimmiyar rawar da ya ke takawa wajen ciyar da kasar gaba, ta hanyar bunkasa masana’antu.
Shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da mataimakinsa Kashim Ibrahim Shettima za su kashe Naira Miliyan dubu tara da ɗari uku da sittin (9,360) a kayan maƙulashe da tafiye-tafiyen cikin gida da waje a baɗi.
Shugaba Bola Ahmed Tinubu, ya jinjinawa wa ’yan Najeriya ya kuma tabbatar musu da cewa sadaukarwarsu za ta haifar da sakamako mai tasirin gaske nan ba da jimawa ba.