Tinubu Ya Gana Da Shugaban Brazil Lula

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya gana da takwaransa na Brazil, Luiz Inacio Lula da Sailva a birnin Brasilia bayan shugaban na Najeriya ya isa ƙasar.

Shugabannin biyu za su tattauna inganta haɗakar diflomasiyya da sauran abubuwan da suka ce zai amfani ƙasashen biyu.

A wata sanarwa da mai magana da yawun shugaban Najeriya Bayo Onanuga ya fitar, ya ce akwai alaƙa mai kyau tsakanin Najeriya da Brazil, inda ya ce a watan Maris na 2025, ƙasashen biyu sun ƙulla yarjejeninyar inganta noma da kasuwanci da tsaro da makamashi da ilimi da ma’adinai.

Post masu alaƙa

Fursuna ya tsere bayan hatsarin motar jami’ai a Yobe

Katsina ta kafa kotunan tafi da gidan ka don gaggauta hukunta ’yan ta’adda

‘Talauci ya faɗo daga kaso 91 zuwa 41 a jihar Sokoto