Me ya sa wasu ƴan Kannywood ke fita daga Triple R mai tallata Tinubu?

A baya-bayan wasu jaruman Kannywood na ci gaba da ficewa daga wata ƙungiyar da wasu ƴan masana’antar suka kafa da nufin tallata Shugaba Tinubu da jam’iyyarsa ta APC gabanin zaɓen 2027.

Mutum na baya-bayan nan da ya sanar da ficewarsa daga ƙungiyar Triple R Kannywood for Renewed Hope, shi ne fitaccen jarumi Rabiu Rikadawa, wanda ya ce ya fita daga ƙungiyar saboda abin da ya kira ”rashin tabbas da rashin aiki da dokokin ƙungiya”.

Kafin Rikadawa an ga wasu fitattun jarumai da suka sanar da ficewarsu daga ƙungiyar, irin su Mansura Isa da fitaccen marubucin nan Ibrahim Birniwa da Yusuf Sasen fitaccen jarumi a masana’antar.

Post masu alaƙa

An gabatar da jirage marasa matuƙa na ARCO Worldwide Services Limited domin ƙarfafa aiyukan tsaro a Arewa maso Yammancin Nijeriya.

An karrama Muhammad Babandede, OFR, OCM, da wasu kungiyoyi kan aiyukan jin kai ga marasa galihu.

Malaman KASU kimanin 200 ne suka bar jami’ar – ASUU