An Roƙi Shugaba Tinubu Ya Taimaki Talakawan Najeriya 

Asusun Bada Lamuni na Duniya (IMF), ya buƙaci Gwamnatin Najeriya ƙarƙashin jagorancin shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da cewa manufofin tattalin arziƙin ƙasar sun kare muradun mutane masu ƙaramin ƙarfi.

Daraktar Hulɗa da Jama’a na IMF Julie Kozack ce ta bayyana hakan a yayin wata ganawa da manema labarai a Washington, D.C babban birnin Amurka.

Julie ta jaddada muhimmancin bai wa talakawan Najeriya masu fama da ƙuncin rayuwa tallafin kuɗi sakamakon sauye-sauyen tattalin arziƙin da gwamnatin shugaba Tinubu ta bijioro da su.

 

 

 

 

Post masu alaƙa

Tinubu Ya Sha Alwashin Ceto Ɗalibai Da Malaman Da Aka Sace A Oyo Da Borno

Kwamishinan ƴan sandan Kano, CP I.A. Bakori ya gargaɗi dakarunsa su guji shiga harkokin siyasa.

Alhazan Kebbi Rukunin Farko Sun Dawo Gida