An Roƙi Shugaba Tinubu Ya Taimaki Talakawan Najeriya 

Asusun Bada Lamuni na Duniya (IMF), ya buƙaci Gwamnatin Najeriya ƙarƙashin jagorancin shugaba Bola Ahmed Tinubu ya tabbatar da cewa manufofin tattalin arziƙin ƙasar sun kare muradun mutane masu ƙaramin ƙarfi.

Daraktar Hulɗa da Jama’a na IMF Julie Kozack ce ta bayyana hakan a yayin wata ganawa da manema labarai a Washington, D.C babban birnin Amurka.

Julie ta jaddada muhimmancin bai wa talakawan Najeriya masu fama da ƙuncin rayuwa tallafin kuɗi sakamakon sauye-sauyen tattalin arziƙin da gwamnatin shugaba Tinubu ta bijioro da su.

 

 

 

 

Post masu alaƙa

Yar Najeriya ta kammala jami’ar Burtaniya da daraja ta daya (1st Class) a ilimin kimiyar samar da manhajar kasuwancin zamani.

Gwamnati ta buƙaci jama’a su guji taɓa kumfar da ta ɓulla a hanyar Kaduna-Abuja

A riƙa yi wa masu shirin aure gwajin miyagun ƙwayoyi :- Buba Marwa