tsaro

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu Ya Ce Za Su Kawo Karshen Ta’addanci

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce gwamnatinsa na tattaunawa da sauran ƙasashen duniya “ta hanyar difilomasiyya” game da matsalolin tsaron da ƙasar ke fuskanta a yanzu. Kalaman shugaban na zuwa ne a lokacin da Shugaban Amurka Donald Trump ke barazanar kutsawa Najeriyar domin kai wa ‘yanbindiga hare-hare bayan ya zargin gwamnatin Tinubu da ƙyale su […]

Read more

Sojojin Najeriya Sun Musanta Miƙa Wuyan Bello Turji

Shelkwatar tsaron Najeriya ta musanta rahotanni da ke cewa riƙaƙƙen ɗan fashin dajin nan wanda ya yi ƙaurin suna, Bello Turji ya miƙa wuya ga sojojin ƙasar. Daraktan yaɗa labarai da aikace-aikacen shelkwatar tsaron, Manjo-Janar Markus Kangye ne ya bayyana haka yayin tattaunawa da manema labarai a yau Alhamis. “Maganar ita ce Bello Turji bai […]

Read more