Sojojin Najeriya Sun Musanta Miƙa Wuyan Bello Turji

Shelkwatar tsaron Najeriya ta musanta rahotanni da ke cewa riƙaƙƙen ɗan fashin dajin nan wanda ya yi ƙaurin suna, Bello Turji ya miƙa wuya ga sojojin ƙasar.

Daraktan yaɗa labarai da aikace-aikacen shelkwatar tsaron, Manjo-Janar Markus Kangye ne ya bayyana haka yayin tattaunawa da manema labarai a yau Alhamis.

“Maganar ita ce Bello Turji bai miƙa wuya ba, muna ci gaba da farautarsa,” in ji shi.

Ana zargin Turji wanda ake nema ruwa a-jallo da kai hare-hare kan al’ummomi a yankin arewa maso yamma, musamman jihohin Zamfara da Sokoto.

A baya-bayan nan, rahotanni sun bayyana cewa ɗan bindigar ya ajiye makamansa, kuma ya saki mutum 32 da yake garkuwa da su, bayan tattaunawar zaman lafiya da malaman addini suka jagoranta a jihar Zamfara.

Post masu alaƙa

Nafi’u ya gargaɗi Atiku ya daina sukar Tinubu da sunan ADC

Yan Sandan a Kano sun kama mutane 244, ciki har da 117 da ake zargi da fadan daba.

Ƴansanda sun ƙara tsaurara matakan tsaro a bikin Takutaha, tare da gargaɗin masu yunkurin tada zaune tsaye.