Jami’an hukumar kashe gobara reshen jihar Kano da kuma na gwamnatin tarayya sun samu nasarar shawo kan gobarar data tashi a jami’ar Northwest dake jihar .
Shugaban hukumar kashe gobara na jihar Kano, Sani Anas , ne ya tabbatar da hakan, lokacin da yake yi wa manema labarai karin haske kan musabbabin tashin gobarar.
Anas, ya ce ‘’sun hangi hayaki da misalin karfe 11 da minti 20am na safe daga ofishinsu, inda daya daga cikin jami’an su ya tabbatar da cewa gobara ce ta tashi a jaim’ar northwest.
Ya kara da cewa wutar ta tashi ne sakamakon tartatsin wutar lantarki, inda wutar ta lalata kayayyakin dake haw ana 9 da kuma taba wasu sassa a haw ana goma a ginin jami’ar.
Shugaban jami’ar Northwest, Farfesa Muktar Atiku Kurawa, ya ce jami’ar tana da tsari na kashe wutar lantarki duk lokacin da aka tashi da aiki, domin sun yi hutun salla babu dalibai a makaranta
Kurawa ya kara da cewa ba zuwa yanzu ba za su iya tantance girman asarar da suka yi, har sai jami’an hukumar sun tabbatar musu da cewa babu wata matsala sannan za su shiga don duba irin abubuwan da aka yi asara.
Ba a samu asarar rai ba, in banda mutum daya dake aiki a jami’ar da ya galabaita sakamakon shakar hayaki da yayi , har aka mika shi zuwa aisibiti don kula da lafiyarsa.