Home » Manyan Jami’an Yan Sanda 3 Sun Sami Karin Girma A Kano

Manyan Jami’an Yan Sanda 3 Sun Sami Karin Girma A Kano

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Kwamishinan yan sandan jihar Kano, CP Ibrahim Adamu Bakori, ya bukaci jami’an yan sandan , da suka samu Karin girma, su kara jajircewa wajen gudanar da aiyukansu domin  nauyi ne ya karu kamar yadda suka yi alkawarin kare rayuwa da dukiyoyin al’umma.

CP Ibrahim Bakori,  ya bayyana hakan ne , a lokacin da yake likawa jami’an Karin girman, wanda aka gudanar a wajen shekatawar manyan jami’an yan sanda dake unguwar Bompai Kano.

Kakakin rundunar rundunar yan sandan jihar Kano, SP Abdullahi Haruna Kiyawa, ta cikin wata sanrawa da fitar ya ce hukumar kula da aiyukan yan sanda ta kas ace ta amince da karin girman tun a ranar 20 ga watan Maris 2025 daga mukamin CSP zuwa ACP wato mataimakan kwamishinan yan sanda.

intervi

Wadanda suka samu karin girman sun hada da ACP Ahmad Munir Tudun Wada, ACP Bashir Kachalla ,
da kuma ACP Umar Mohammed Alkali.

Bakori, ya godewa babban sufeton yan sandan Nijeriya da kuma hukumar kula da aikin yan sanda ta kasa, bisa karin girman da aka yi jami’an saboda jajircewarsu.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?