Tauraron dan kwallon kafa na kasar Ghana Asamoah Gyan ya sanar da rataye takalminsa.

Dan kwallon kafa na kasar Ghana Asamoah Gyan ya sanar da rataye takalminsa

Tauraron dan kwallon kafa na kasar Ghana Asamoah Gyan ya sanar da rataye takalminsa.

A wani saƙon tuwita, Gyan ya ce “Lokaci ya yi da za a rataye riga da takalma yayin da na yi ritaya daga wasan kwallon kafa.”

Dan wasan na gaba ya ci kwallaye 51 a wasanni 109 da ya buga wa ƙasar, abin da ya sa ya zama dan wasan da ya fi cin kwallaye a tarihin Ghana.

Dan wasan mai shekaru 37, ya fara buga wasa a matakin ƙungiya ne a shekara ta 2003, inda ya buga wasa a kungiyar farko ta Ghana, Liberty Professionals, sannan ya buga wasa a Turai a Udinese ta Italiya da Rennes na Faransa da kuma Sunderland ta Premier ta Ingila.

Ya taba buga wasa a Haɗaɗɗiyar Daular Larabawa, a kungiyar Al Ain, ya kuma taimaka wa ƙungiyar ta lashe kofin babbar gasar ƙasar ta Pro-League sannan kuma ya zama dan wasan da ya fi cin kwallaye inda ya zura kwallaye 28 a wasanni 32.

A Ghana, Gyan ya yi fice a babbar tawagar kasar, Black Stars, a gasar cin kofin duniya ta Fifa guda uku – a 2006, 2010 da 2014.

Shi ne dan wasan da ya fi cin kwallaye a gasar cin kofin duniya a Afirka, inda ya ci kwallaye shida.

Ya buga wa ƙasarsa wasanni bakwai na gasar cin kofin nahiyar Afirka, inda Black Stars ta ƙare a matsayi na uku a shekara ta 2008 sannan a matsayi na biyu a 2010 da 2015.

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *