Tinubu Ya Naɗa Sabon Minista

Shugaba Bola Tinubu ya naɗa Dokta Bernard Mohammed Doro daga Jihar Filato a matsayin sabon Minista a gwamnatinsa.

Mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwar da fitar a wannan Talatar, inda ya ce naɗin zai tabbata ne bayan amincewar Majalisar Dattawa.

Naɗin Dokta Doro na zuwa ne bayan zaben Farfesa Nentawe Goshwe Yilwatda da aka yi a matsayin Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa a watan Yuli, wanda a baya yake riƙe da muƙamin Ministan Harkokin Jin Kai da Rage Talauci.

Kazalika, sanarwar ta ce tuni an miƙa wa Majalisar Dattawa sunan sabon ministan domin tantancewa.

Post masu alaƙa

An kashe mutum saboda Naira 200 a Ogun

Masu ruwa da tsaki na APC a jihar Akwa Ibom sun yi watsi da tsarin tsayar da ɗan takara ta maslaha

Makarantar kurame ta Katsina ta lashe gasar wasannin guragu ta gwamna Radda