Tinubu Ya Naɗa Sabon Minista

Shugaba Bola Tinubu ya naɗa Dokta Bernard Mohammed Doro daga Jihar Filato a matsayin sabon Minista a gwamnatinsa.

Mai magana da yawun shugaban kasar, Bayo Onanuga, ne ya bayyana hakan cikin wata sanarwar da fitar a wannan Talatar, inda ya ce naɗin zai tabbata ne bayan amincewar Majalisar Dattawa.

Naɗin Dokta Doro na zuwa ne bayan zaben Farfesa Nentawe Goshwe Yilwatda da aka yi a matsayin Shugaban jam’iyyar APC na ƙasa a watan Yuli, wanda a baya yake riƙe da muƙamin Ministan Harkokin Jin Kai da Rage Talauci.

Kazalika, sanarwar ta ce tuni an miƙa wa Majalisar Dattawa sunan sabon ministan domin tantancewa.

Post masu alaƙa

Gwamnatin Jigawa ta kashe kusan naira biliyan bakwai (7) domin tallafa wa ma’aikata ta fuskar noma

Jami’an tsaro sun ceto ɗalibai da malaman da aka sace a Kogi

Hukumomin tsaro sun kama wanda ya kirkiri hukumar bogi a Nijeriya