Home » Tinubu ya rantsar da mai riƙon muƙamin gwamnan jihar Rivers

Tinubu ya rantsar da mai riƙon muƙamin gwamnan jihar Rivers

by Mujahid Wada Guringawa
0 comment

Shugaban Najeriya, Bola Tinubu ya rantsar da Vice Admiral Ibok-Ete Ekwe Ibas, mai ritaya a matsayin gwamnan riƙo na jihar Rivers, bayan ƙaƙaba dokar ta-ɓaci a jihar, jiya Talata.

Bukin rantsuwar ya gudana ne yau Laraba a fadar shugaban Najeriyar da ke Abuja.

A ranar Talatar ne Tinubu ya sanar da sunan Ibas a matsayin wanda zai riƙe muƙamin gwamnan jihar ta Rivers, bayan dokar ta-ɓaci da ya ƙaƙaba wa jihar, lamarin da ke nufin an dakatar da gwamna Siminalayi Fubara da mataimakiyarsa da kuma ƴanmajalisar dokokin jihar na tsawon wata shida.

Jihar Rivers ta kwashe tsawon lokaci cikin rikita-rikitar siyasa, lamarin da ya kai ga yunƙurin tsige gwamnan jihar da kuma rushe zauren majalisar dokokin jihar.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?