Tinubu Ya Yi Farin Ciki Da Ricikin Jam’iyun Adawa

Shugaban Najeriya Bola Tinubu ya ce yana farin ciki da halin rikici da jam’iyyun adawa da dama na ƙasar ke ciki.

Shugaban ya bayyana haka ne a lokacin jawabin da ya yi na ranar tunawa da dimokuraɗiyya a zauren majalisar dokokin ƙasar da ke Abuja, yau Alhamis.

“Ina jin daɗin ganin jam’iyyun adawa a tagayyare,” kamar yadda shugaban ƙasar ya bayyana a jawabinsa na ranar dimokuraɗiyya.

Tinubu ya ce “ba zan ce ina so na ga kun gyaru ba, ina ma jin dadin ganin ku a haka.

Hakan na zuwa ne yayin da jam’iyyar APC mai mulkin ƙasar ke ci gaba da karɓar ƴan siyasa masu sauya sheƙa daga jam’iyyun adawa zuwa cikinta.

Tinubu ya ce jam’iyyar APC ba za ta hana kowa shiga cikinta ba domin yin hakan tauye hakkin al’umma ne.

Post masu alaƙa

Gwamna Namadi ya dakatar da hadimansa huɗu

Ƴan sanda sun fara bincike kan mutuwar wanda ake zargi da sokawa matashi Wuƙa a Kano

Babachir Lawal ya fita daga ADC