Uwargidan shugaban Najeriya Sanata Oluremi Tinubu ta kaddamar da rumbum abinci (National Community Food Bank Programme ) ga jama’ar yankin kudu maso kudancin Najeriya a Kalaba, baban birnin jihar Ribas.
Sanata Remi ta kaddamar da rumbun abincin ne da niyyar tallafawa yara ‘yan kasa da shekaru shida da mata masu juna biyu.
An kaddamar da shirin ne a ranar Juma’a 4 ga Satumba, 2026 kamar yadda kamfanin dillacin labaran Najeriya NAN ya rawaito.
Yayin kaddamar da rumbun, Uwargidan shugaban Najeriya ta ce haka ya dace da tsarin shugaba Tinubu na sabunta fatan ‘yan Najeriya wurin yaki da ta’addanci da inganta lafiya da kuma bunkasa walwala da jin dadin jama’a
