Home » Wani sanata daga Kano ya raba wa dalibai 200 tallafin kudin makaranta

Wani sanata daga Kano ya raba wa dalibai 200 tallafin kudin makaranta

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Wani sanata daga Kano ya raba wa dalibai 200 tallafin kudin makaranta

Daliban jami’ar Bayero su 200 sun sami tallafin kudin makaranta da Sanatan Kano ta tsakiya sanata Rufa’i Sani Hanga ya biya musu.

Wannan na zuwa ne yayin da ɗalibai ke neman ɗauki daga gwamnati da masu hannu da shuni domin biyan kudin makaranta.

Ya zuwa yanzu dai rahotanni sun nuna cewa, ‘yan majalisun tarayya na Bichi da Dambatta/Makoda da Wudil/Garko ne suke kan gaba wajen  biya wa daliban yankinsu kudin makaranta bayan ƙarin kudin makaranta da jami’o’i suka yi.

Dalibai da dama na cikin fargabar gaza cigaba da karatun jami’a a sassan Kano bisa rashin kudin da za su biya kudin makarantunsu tun bayan karin kudin da aka yi.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?