Wasu matasa sun kai wa tsohon ministan labarai, Labaran Maku, hari a jihar Nasarawa

Wasu dauke da muggan makamai da ake zargin masu garkuwa da mutane ne sun kai hari zuwa gidan tsohon ministan yada labarai, Labaran Maku da ke yankin Ola a karamar hukumar Akwanga da ke jihar Nasarawa.

Uku daga cikin jami’an tsaron da suke aikin tsaro gidan sun gamu da munanan raunuka a sakamakon harin da ‘yan bindigan suka kai a ranar Asabar.

A cewar daya daga cikin masu tsaron, maharan sun yi ta kokarin kutsa kai zuwa cikin gidan amma sun gamu da tirjiya daga masu tsaron gidan.

A sanarwar da mai dafa masa kan harkokin hulda da jama’a, Mr Peter Ahemba a jiya Lahadi cikin wata sanarwa ya misalta harin a matsayin mummunar lamarin da ba za su lamunta ba.

Ya ce tunin gwamnan ya umarci jami’an tsaro da su farauto maharan tare da tabbatar da gurfanar da su.

Post masu alaƙa

Barista Hamza Ɗantani ya jinjinawa CP Bakori da wasu kwamishinonin yan sanda biyu.

Rundunar yan sandan jihar Kano ta ceto fasinjoji 9 bayan musayar wuta da yan bindiga a hanyar Doguwa.

Kwalejin Fasaha ta Kogi ta dakatar da lakcarori 7 kan cin zarafin ɗalibai