An kama mutum 4 kan damfarar maniyyata a Kebbi
Wasu mutum huɗu da ake zargi da damfarar maniyyata aikin Hajjin bana sun shiga hannu a Jihar Kebbi. Jami’in hulɗa da jama’a na Rundunar ’Yan Sandan Jihar Kebbi ta, SP Bashir Usman, ya bayyana cewa dubun waɗanda ake zargin ta cika ne bayan ƙorafe-ƙorafe daga waɗanda abin ya shafa da kuma Hukumar Jin Daɗin Alhazai […]










