• Home  
  • Jirgin karshe na maniyyata aikin hajjin bana daga kasar Nijar ya sauka a kasar saudiyya
- Kasashen Ketare - Labarai

Jirgin karshe na maniyyata aikin hajjin bana daga kasar Nijar ya sauka a kasar saudiyya

Dan gane da aikin Hajjin bana dai, rahotonnin daga Jamhuriyar Nijar na tabbatar da cewa Jirgin ƙarshe na maniyyatan kasar ya isa ƙasa mai tsarki wato Saudiyya.

Jirgin karshe na maniyyata aikin hajjin bana daga kasar Nijar ya sauka a kasar saudiyya

Dan gane da aikin Hajjin bana dai, rahotonnin daga Jamhuriyar Nijar na tabbatar da cewa Jirgin ƙarshe na maniyyatan kasar ya isa ƙasa mai tsarki wato Saudiyya.

Wanda alƙaluma suka nuna cewa Jimillar mutune 15,891 ne za su yi aikin Hajji na bana daga Jamhuriyar ta Nijar .

Sai dai akwai wasu mutane da dama da ba za su damar zuwa gudanar da ibadar ba duk da cewa sun biya kuɗinsu ta hannun wasu kamfanonin shirya aikin hajji da Umarah.

Ana samun matsalolin rashin samun tafiyar maniyyata, sakammakon wasu dalilai mabambanta, a wasu ƙasashe da suka haɗa da Nijeriya, wanda hakan yake baƙanta ran maniyyata.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai