• Home  
  • Wike Ya Kwace Filin Sakatariyar PDP A Abuja
- Babban Labari

Wike Ya Kwace Filin Sakatariyar PDP A Abuja

  Ministan birnin tarayya Abuja Nyesom Wike, ya kwace filin sabuwar sakatariyar jam’iyyar PDP ta kasa dake birnin tarayya Abuja sakamakon rashin biyan haraji na shekaru 20. Bayanin hakan na cikin wata wasikar da hukumar kula da ƙasa ta birnin tarayya Abuja ta aikewa jam’iyyar PDP, dauke da kwanan watan 13 ga watan Maris. Daraktan […]

 

Ministan birnin tarayya Abuja Nyesom Wike, ya kwace filin sabuwar sakatariyar jam’iyyar PDP ta kasa dake birnin tarayya Abuja sakamakon rashin biyan haraji na shekaru 20.

Bayanin hakan na cikin wata wasikar da hukumar kula da ƙasa ta birnin tarayya Abuja ta aikewa jam’iyyar PDP, dauke da kwanan watan 13 ga watan Maris.

Daraktan sashin kula da ƙasa na Abuja Chijioke Nwankwoeze, ne ya sanya hannu akan wasikar a madadin minista Wike.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai