Ya kamata a yi takatsantsan wajen ba wa Ganduje shugabancin APC ~ Dokta Salihu Lukman

Tsohon mataimakin shugaban jam’iyar APC na ƙasa shiyyar arewa maso yamma  Dokta Salihu Lukman, ya ƙara jaddada cewa take-taken neman ɗora tsohon gwamnan Kano Abdullahi Ganduje a matsayin shugaban jam’iyar na ƙasa, ya saɓa wa dokokin jam’iyar ƙarara.

Haka kuma Dokta Lukman ya bayar da hujjojin cewa akwai fa maganar duba sanin ya kamata da ɗabi’u na gari kafin a ce za a naɗa Ganduje shugaban jam’iyar APC na ƙasa.

Dokta Lukman ya yi kira ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya nisanta kansa da duk wata ƙumbiya-ƙumbiyar neman naɗa Ganduje shugaban jam’iyar APC.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr