Home » Yadda Aka Dakatar Da Sheikh Bin Uthman Daga Limancin Masjid Sahaba

Yadda Aka Dakatar Da Sheikh Bin Uthman Daga Limancin Masjid Sahaba

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga:Mujahid Wada Musa

Masallacin Jami’ur Rahman, wanda a da ake kira da Masjid Sahaba, ya dakatar da Sheikh Muhammad Bin Uthman daga limanci biyo bayan hudubar da ya yi a ranar 24 ga watan Janairu.

Asalin masallacin, wanda Bin Uthman ke jagoranta tsawon shekaru 24, na kusa da sabon wanda AY Maikifi ya sayi filin.

Bayan Maikifi ya samu mallakar filin a hannun gwamnati don gina sabon masallacin Sahaba, sai ya tuntubi Bin Uthman inda suka amince da cewa tsohon masallacin Sahaba zai dawo sabon gini.

Sai dai kuma a yayin huɗubar da ya yi a ranar 24 ga watan Janairu, wacce ta haifar cece-ku-ce, Bin Uthman ya ba da labarin yadda aka rage masa matsayi wajen gudanar da harkokin masallacin.

A cewar sa, an nada shugabanni uku masallacin amma ba a nada shi a jagora ba.

Daily Nigerian ta gano cewa huɗubar ta ranar 24 ga watan Janairu ta fusata masallata, inda suka kusa dukan sakataren kwamitin amintattu na masallacin, Abdulkadir Isawa.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?