• Home  
  • Yadda Aka Dakatar Da Sheikh Bin Uthman Daga Limancin Masjid Sahaba
- Babban Labari - Labarai

Yadda Aka Dakatar Da Sheikh Bin Uthman Daga Limancin Masjid Sahaba

Masallacin Jami’ur Rahman, wanda a da ake kira da Masjid Sahaba, ya dakatar da Sheikh Muhammad Bin Uthman daga limanci biyo bayan hudubar da ya yi a ranar 24 ga watan Janairu.

Daga:Mujahid Wada Musa

Masallacin Jami’ur Rahman, wanda a da ake kira da Masjid Sahaba, ya dakatar da Sheikh Muhammad Bin Uthman daga limanci biyo bayan hudubar da ya yi a ranar 24 ga watan Janairu.

Asalin masallacin, wanda Bin Uthman ke jagoranta tsawon shekaru 24, na kusa da sabon wanda AY Maikifi ya sayi filin.

Bayan Maikifi ya samu mallakar filin a hannun gwamnati don gina sabon masallacin Sahaba, sai ya tuntubi Bin Uthman inda suka amince da cewa tsohon masallacin Sahaba zai dawo sabon gini.

Sai dai kuma a yayin huɗubar da ya yi a ranar 24 ga watan Janairu, wacce ta haifar cece-ku-ce, Bin Uthman ya ba da labarin yadda aka rage masa matsayi wajen gudanar da harkokin masallacin.

A cewar sa, an nada shugabanni uku masallacin amma ba a nada shi a jagora ba.

Daily Nigerian ta gano cewa huɗubar ta ranar 24 ga watan Janairu ta fusata masallata, inda suka kusa dukan sakataren kwamitin amintattu na masallacin, Abdulkadir Isawa.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai