Home » HISBA Ta Kama Matasan Da Suka Daurawa Kansu Aure

HISBA Ta Kama Matasan Da Suka Daurawa Kansu Aure

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Daga: Safiyanu Haruna Kutama

Hukumar Hisba ta jihar Kano ta kama wasu matasa biyu mace da Namiji da suka daurawa kansu aure a gidan cin abinci da shakatawa na Banana dake unguwar Zoo road a cikin birnin Kano.

Mataimakin kwamandan Hisba na Jihar Kano a bangaren kai sumame da ayyukan yau da kullum Dr Mujahideen Amenuddeen shine ya shaida hakan ga manema labarai a birnin Kano.

Yace bayan samun labarin daura auren a gidan cin abinci ba tare da waliyansu ba ,sai suka dana tarko domin kamasu ,saboda suna yawan zuwa wajen shakatawa bayan daura auren nasu.

Dr Mujahideen ya shaidawa kafar yada labarai ta VOA cewa sun kama ma’auratan ne a cikin daren ranar Laraba lokacin da sukaje wajen shakatawa.

Mataimakin kwamandan Hisbar yace abinda sukayi ya saba da shari’a kuma abin takaici ne, ace an daura aure babu ko daya daga wakilcin iyaye ko ‘yan uwa sai dai wakilcin abokai kawai wadanda ma duka kazo nazo ne.

A yanzu haka matasan mace da namijin suna hannun HISBA domin gudanar da bincike.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?