Home » ‘Yan Majalisar Tarayya Sun Amince Wa Buhari Karɓo Bashin Dala Miliyan 800

‘Yan Majalisar Tarayya Sun Amince Wa Buhari Karɓo Bashin Dala Miliyan 800

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Majalisar Wakilai

Ƴan majalisar tarayya sun amince wa shugaba Muhammadu Buhari, ya karɓo bashin dala miliyan $800m.

Mamban kwamitin kula da karɓo bashi a majaliaar wakilai, Abubakar Yunusa Ahmad ne ya bayya na hakan a jiya Jumu’a a hirarsa da manema labarai.

Ɗanmajalisar ya ce, sun kafa sharaɗin ba zasu bari gwamnatin Buhari mai barin gado ta kashe kuɗin baki ɗaya ba.

Haka kuma gwamnatin zababben shugaban ƙasa da ke dab da kama aiki tana da haƙƙin kawo na ta tsarin yadda bashin zai amfani ‘yan Najeriya.

Tun da farko, shugaba Buhari ya aike da takarda ga majalisar dattawa, yana neman su amince ya kara sunkuto bashin dala miliyan $800m daga bankin duniya.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?