Home » ‘Yan Sandan Najeriya Sun Janye Gayyatar Sarki Muhammadu Sunusi II

‘Yan Sandan Najeriya Sun Janye Gayyatar Sarki Muhammadu Sunusi II

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta janye gayyatar da ta yi wa Sarkin Kano na 16 Malam Muhammadu Sunusi II. 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
KANO

Rundunar ‘Yan Sandan Najeriya ta janye gayyatar da ta yi wa Sarkin Kano na 16 Malam Muhammadu Sunusi II. 

Wannan na ƙushe a cikin wata sanarwar da Rundunar ta fitar da jami’in hulɗa da jama’a na ƙasa ACP Olumuyiwa Adejobi ya sanya wa hannu.

Sanarwar ta ce rundunar ta janye gayyatar ne biyo bayan shawarar da masu ruwa da tsaki suka basu da kuma gudun kar a yi wa aikin rundunar mummunar fahimta ko kuma a mayar da batun siyasa.

Maimakon sarkin ya je Abuja domin amsa tambayoyin rundunar, Sufeton ‘yan sanda na na ƙasa Kayode Egbetokun ya umarci ‘yan sandan da ke sashen tattara bayanan sirri su je Kano domin jin ta bakin Sarkin dangane da abin da ya faru a lokacin bukukuwan ƙaramar sallah.

Bayyanar wannan sanarwa ta janyo mabanbanta martani daga ‘yan Najeriya a kafafen sada zumunta.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?