Home » ‘Yan takarar shugabancin Najeriya 3 na shirin samar da jam’iyya guda daya

‘Yan takarar shugabancin Najeriya 3 na shirin samar da jam’iyya guda daya

by Hassan Abdu Mai Bulawus
0 comment
'Yan takarar shugabancin Najeriya 3 na shirin yin samar da jam'iyya guda daya

Ƴan takarar shugaban ƙasa na jam’iyyun PDP,  da NNPP, da kuma Leba,  wato Atiku Abubakar, da Rabiu Musa Kwankwaso, da Peter Obi sun fara tattaunawa kan yiwuwar haɗewa da manufar kafa babbar jam’iyya ɗaya wadda za ta yi hamayya da jam’iyyar APC mai mulki.

Wata majiya ta ce, Kwankwaso da Atiku ne suka fara tattaunawa daga bisani suka shigar da Peter Obi.

Sai dai ba su tattauna wanda zai jagoranci jam’iyyar hamayyar da za su kafa ba, saboda suna jiran hukuncin da kotun sauraren ƙarar shugaban ƙasa za ta yanke.

Shugabannin jam’iyyun uku suna fata kotun za ta soke zaɓen Tinubu kuma ta sa a sake zaɓe.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?