Home » Zaɓe: Wani Shugaban Majalisa Ya Sha Kaye a Hannun Wani Matashi

Zaɓe: Wani Shugaban Majalisa Ya Sha Kaye a Hannun Wani Matashi

Yobe/Sakamakon Zaɓen

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Bayan ya shafe shekara 20 a Majalisa, Shugaban Majalisar Dokokin Jihar Yobe, Ahmed Mirwa Lawan, ya sha kaye a hannun matashi mai shekaru 35.

Lawan, na jam’iyyar APC dai ya sha kayen ne a hannun Lawan Musa na jam’iyyar PDP a mazabar Nguru II.

Wannan shi ne karo na biyu matashin ke fafatawa da kakakin majalisar, sai a wannan karon ne ya samu nasarar lashe zaben.

Kamar yadda jami’in tattara sakamakon zaben wannan mazaba ta Nguru Dr Habib Muhammad ya bayyana cewar,

Dan takarar Jam’iyyar ta PDP Musa Lawan ya kada kakakin majalisar Hon Ahmad Lawan Mirwa, ne da Kuri’u, da ƙuri’u dubu shida da ɗari shida da arba’in da takwas, yayin da shi kakakin majalisar dokokin ya samu Kuri’u dubu shida da ɗari huɗu da sittin da shida

Wata majiya da ke garin na Nguru ta bayyana wa majiyarmu cewa, an so a samu ‘yar hatsaniya a wannan mazaba ta Nguru sakamakon kokarin yin jinkiri shelanta wanda ya ci zaben,

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?