Zaɓaɓɓen Shugaban Ƙasar Najeriya Ya Dawo Daga Ziyarar da Ya Kai Faransa

Zaɓaɓɓen shugaban Najeriya Bola Ahmed Tinubu ya dawo ƙasar nan bayan wata ziyara da ya kai ƙasar Faransa inda ya shafe tsawon mako biyar.

A baya an bayyana cewa, dalilin tafiyar shi ne samun hutu bayan kammala yaƙin neman zaɓen da zaɓen da aka gudanar da ya tabbatar da shi a matsayin shugaban ƙasa mai jiran gado.

Tun farko an tsara cewa zaɓaɓɓen shugaban na Najeriya zai kwan biyu a Paris cikin ƙasar Faransa, daga nan kuma ya wuce zuwa birnin London, kafin ya dangana da ƙasar Saudiyya.

Sai dai rashin ganin sa a ƙasar Saudiyya lokacin aikin umrah, musamman daidai lokacin da shugaban ƙasar mai barin gado, Muhammadu Buhari yake can, ya haifar da jita-jita da raɗe-raɗi.

Tinubu ya sauka ne da yammacin a yau a filin jirgin sama na Nnamdi Azikiwe, da ke Abuja babban birnin ƙasar nan.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr