Zaben Kogi: Ɗan takarar gwamna ya zargi INEC da yi masa wala-wala

Dan takarar gwamnan jihar Kogi na jam’iyyar PDP, Sanata Dino Melaye, ya gabatar da jawabi ga manema labarai ana tsaka da kaɗa ƙuri’a a zaɓen gwamnan jihar.

Ana gudanarwa a wannan zaɓe ne a yau Asabar, inda ya zargi hukumar zaɓe mai zaman kanta ta ƙasa INEC da yunkurin yi masa wala-wala.

Melaye ya ce dole INEC ta soke sakamakon zaɓen ƙananan hukumomi guda biyar, wadanda suka hada da Okene, Okehi, Ajaoukuta, Adavi da kuma Ogori/Mangogo.

Post masu alaƙa

Gwamnan Kano ya naɗa Barista Hafsat Kutama shugabar hukumar PCACC

Rundunar yan sandan Kano ta kama mutane 10 da ake zargi da satar motoci tsakanin jihohi.

Ba za mu dawo da tallafin man fetur ba —Fadar Shugaban Ƙasa