• Home  
  • Zaɓe: Kotu ta soke nasarar da gwamnan Nassarawa ya samu
- Labarai

Zaɓe: Kotu ta soke nasarar da gwamnan Nassarawa ya samu

Kotun sauraron ƙararraki zaɓen gwamnan Kano a jihar Nassarawa, ta umarci hukumar zaɓen jihar da ta janye shaidar samun nasarar lashe zaɓen gwamnan da Injiniya Abdullahi Sule na jam’iyyar APC ya yi a zaɓen da aka yi na ranar 19 ga watan Maris ɗin shekarar da muke ciki.

Zaɓe: Kotu ta soke nasarar da gwamnan Nassarawa ya samu

Kotun sauraron ƙararraki zaɓen gwamnan Kano a jihar Nassarawa, ta umarci hukumar zaɓen jihar da ta janye shaidar samun nasarar lashe zaɓen gwamnan da Injiniya Abdullahi Sule na jam’iyyar APC ya yi a zaɓen da aka yi na ranar 19 ga watan Maris ɗin shekarar da muke ciki.

Sannan kotun ta umarci hukumar zaɓen da ta ayyana David Ombugadu na jam’iyyar PDP a matsayin wanda ya samu nasarar.

Wannan umarni ya fito ne daga bakin mai shari’a Ezekiel Ajayi wanda ya bayyana hakan a yau.

A yayin da yake bayyana jin daɗinsa, tsohon shugaban majalisar Dattawan ƙasar nan, Bukola Saraki, ya taya ɗan jam’iyyar tasu ta PDP murnar wannan nasara da ya samu a kotun.

Wannan hukunci na zuwa ne bayan an yi makamancinsa a nan Kano inda kotun ta ayyana Dr. Nasiru Yusuf Gawuna a matsayin wanda ya lashe zaɓen Kano, a maimakon gwamnan Kano, Injiniya Abba Kabir Yusuf wanda tuni ya tabbatar da shirinsa na ɗaukaka ƙara.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai