Home » Zulum Ya Roki ‘Yan Borno Su Tashi Da Azumi Gobe Litinin

Zulum Ya Roki ‘Yan Borno Su Tashi Da Azumi Gobe Litinin

Gwamnan Jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum ya bukaci jama'ar sa su tashi da azumi gobe litinin da adduoi domin neman taimakon Allah.

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Gwamnan Jihar Borno Farfesa Babagana Umara Zulum ya bukaci jama’ar sa su tashi da azumi gobe litinin da adduoi domin neman taimakon Allah.

Gwamnan ya bayyana hakan ne a wani jawabi da ya yi wa ‘yan jihar a Maiduguri a jiya Asabar.

Zulum ya yi alkawarin karfafa rundunonin sa kai, da inganta tattara bayanan sirri a matakin al’umma, da kuma tsarin daukar mataki cikin gaggawa da zarar an ga wani abu da ba aminta da shi ba, a wani yunkuri na dakile matsalar tsaro da ta sake kunno kai a jihar.

Ya ce, “A cikin ‘yan watannin nan, na nemii shawarwari daga abokan huldar mu na tarayya da shugabannin hukumomin tsaro daban-daban, ina mai farin cikin sanar da ku cewa hadin gwiwar da aka samu yanzu tsakanin jihar Borno da gwamnatin tarayya ya fi na kowane lokaci karfi.

“Muna aiki tukuru domin fito da dabarun karfafa tsaro, inganta musayar bayanan sirri, da kuma baiwa jami’an tsaronmu kayan aikin da suka dace don tunkarar barazanar da ke gabanmu,” in ji Zulum.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?