Ƙasar Saudiyya Ta Ja Kunnen Masu Ɗaukar Hoto a Lokacin Ibada

Hukumar kula da aikin Haji da Umrah ta Saudiyya ta yi kira ga masu ziyarar ibada da su guji ɗauke-ɗauken hotuna a yayin gudanar da ibada a wurare masu alfarma.

Hukumar ta ce bai kamata masu ziyarar ibadar su ɓige da ɗaukar hotuna ba a maimakon mayar da hankali kan ibadar da ta kai su ƙasar.

Haka kuma hukumar ta gargaɗi masu ɗaukar hotunan da su guji ɗaukar hoton da fuskokin mutane a cikin hoton nasu ba tare da izini ba.

Sannan ta bayyana cewar masu ziyarar ibadar su daina tsayawa don ɗaukar hoto a wuraren da jama’a da dama ke taruwa, domin a cewarta hakan na janyo cunkuson jama’a a wuraren.

A baya-bayan nan dai mutane sun ɓullo da salon ɗaukar hotuna a lokacin ziyarar Umrah ko Aikin Hajji tare da wallafawa a shafukansu na sada zumunta.

Lamarin da wasu malamai ke ganin cewa yawan yin hakan ka iya zama ‘Riya’, abin da kuma a cewar malaman zai iya ɓata wa mutane niyyar ibadar tasu.

Post masu alaƙa

Kotun kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kwace kadarorin Godwin Emefiele

Dalibai huɗu za su wakilci Najeriya a gasar Spelling Bee ta Duniya a China

Babandede Ya Taya Shettima Murnar Sake Samun Takarar Mataimakin Shugaban Kasa