‘Ƴan sanda sun kama wasu da ake zargin suna yunƙurin kai hari gidan Atiku Abubakar

‘Ƴan sanda sun kama wasu mutane guda huɗu da ake zargin suna yunƙurin kai hari ga gidan tsohon mataimakin shugaban Ƙasa, Atiku Abubakar a birnin Yola.

An fara kama ɗaya daga cikin mutanen ne mai suna Jubrila Mohammed, wanda ya amsa cewa shi mamba ne a kungiyar Boko Haram lokacin da suke yunkurin kai harin da misalin karfe 9 na dare ranar Lahadi.

Wata sanarwa da mai taimaka wa tsohon mataimakin shugaban ƙasar Abdul Rasheed Shehu ya fitar, ta ce an samu nasarar kama abokan haɗin bakinsa guda uku.

Sanarwar ta kara da cewa mutanen da ake zargin sun kuma yi yunkurin kai wa kamfanoni masu alaƙa da Atiku Abubakar a Yola da kuma wasu wurare kafin a kama su.

Zuwa yanzu, an miƙa dukkan mutanen da ake zargi hannun sojoji in ji sanarwar domin ci gaba da bincike.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr