• Home  
  • DSS Ta Kai Sumame Hedikwatar SERAP
- Babban Labari - Labarai

DSS Ta Kai Sumame Hedikwatar SERAP

Ƙungiyar SERAP mai fafutikar yaƙi da cin hanci da Rashawa a Najeriya ta ce Jami’an hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (DSS) sun kai samame ofishin su da ke Abuja.

Hukumar DSS ta shawarci gwamnoni da su yi adalci domin ɗorewar zaman lafiya

Ƙungiyar SERAP mai fafutikar yaƙi da cin hanci da Rashawa a Najeriya ta ce Jami’an hukumar tsaron farin kaya ta Najeriya (DSS) sun kai samame ofishin su da ke Abuja.

Sanarwar da kungiyar ta fitar ta kafar X ta zargi jami’an tsaron da yi wa ofishinsu ƙawanya ba bisa ka’ida ba.

SERAP ta ce bayan kawanyar da jami;an na DSS su ka yi wa ofishin nata, sun bukaci ganawa manyan daraktocin ta.

SERAP ta yi kira ga shugaban ƙasa Bola Ahmed Tinubu da ya shiga tsakani kuma ya umarci jami’an DSS ta daina abin da ƙungiyar ta kira ”tsangwama da cin zarafi, da kuma take haƙƙin ‘yan Najeriya”.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000