• Home  
  • Sojoji Sun Kashe Yan Boko Haram 15 A Borno
- Babban Labari - Labarai

Sojoji Sun Kashe Yan Boko Haram 15 A Borno

Rundunar sojin saman Najeriya ta ce ta kashe mayaƙa sama da 15 a wasu hare-haren da ta kai ta sama a maɓuyarsu da ke dajin Sambisa a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya. Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar Air Commodore Ehimen Ejodame ya fitar, ta ce an kai hare-haren ne […]

Rundunar sojin saman Najeriya ta ce ta kashe mayaƙa sama da 15 a wasu hare-haren da ta kai ta sama a maɓuyarsu da ke dajin Sambisa a jihar Borno da ke arewa maso gabashin Najeriya.

Wata sanarwa da mai magana da yawun rundunar Air Commodore Ehimen Ejodame ya fitar, ta ce an kai hare-haren ne a ranar Laraba, 3 ga watan Satumba, a kan mayaƙa da kuma kwamandojin da ake alaƙantawa da wasu hare-haren da aka kai a baya-bayan nan.

Najeriya na fama da rikicin ƙungiyar Boko Haram da ISWAP a tsawon shekara 16, lamarin da ya haifar da asarar dubban rayuka da tarwatsa miliyoyin mutane, wani abu da ya haifar da matsalar jin-ƙai.

A baya-bayan nan al’umma a wasu yankunan jihar Borno sun shiga fargaba sanadiyyar dawowar hare-haren mayaƙan, inda a makon da ya gabata aka ruwaito yadda mayakan suka kashe kimanin mutum takwas.

Harin saman na sojojin Najeriya na zuwa ne bayan “bayanan sirri sun tabbatar da ayyukan mayakan a yankin,” kamar yadda mai maganar ya bayyana.

Ya kuma ƙara da cewa harin ya lalata kayan aikin mayakan Boko Haram da Iswap da dama.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000