• Home  
  • Iran da Amurka sun amince da yarjejeniyar tsagaita wuta
- Babban Labari

Iran da Amurka sun amince da yarjejeniyar tsagaita wuta

Gwamnatin Iran ta bayyana amincewarta da yarjejeniyar tsagaita wuta na makonni biyu a yayin da ake sa ran fara tattaunawar sulhu ranar Juma’a a ƙasar Pakistan. Iran ta kuma sanar da amincewar ta buɗe Mashigar Hormuz gaba ɗaya ne bayan da Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya sanar da dakatar da kai mata hare-hare na […]

Gwamnatin Iran ta bayyana amincewarta da yarjejeniyar tsagaita wuta na makonni biyu a yayin da ake sa ran fara tattaunawar sulhu ranar Juma’a a ƙasar Pakistan.

Iran ta kuma sanar da amincewar ta buɗe Mashigar Hormuz gaba ɗaya ne bayan da Shugaban Ƙasar Amurka, Donald Trump, ya sanar da dakatar da kai mata hare-hare na tsawon makonni biyu.

Hakan na zuwa ne bayan Amurka ta amince da wasu ƙa’idoji 10 da Iran ta gindaya a matsayin sharaɗinta na amince da yarjejeniyar sulhu.

Hukumomin Iran sun bayyana matakin da aka kai a matsayin nasara ga ƙasar, inda suka bayyana cewa sun yi wa al’ummar ƙasar cewa za a ƙulla yarjejeniya ne bisa la’akari da ƙa’idodjin da ƙasar ta shimfiɗa.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai