Tarayyar Turai (EU) ta ware Yuro miliyan 2.3m a matsayin tallafin gaggawa ga Najeriya, Kamaru, Chadi da Jamhuriyar Afirka ta Tsakiya domin taimaka musu wajen daƙile cutar zazzaɓin cizon sauro, kwalara.
Daga cikin kudin, Najeriya za ta samu Yuro miliyan 1.5, wanda za a yi amfani da shi wajen ƙara yawan jami’an da ke aikin daƙile cutar, samar da kayan aikin jinya da kuma inganta samar da ruwa mai tsafta, tsaftar muhalli da kuma tsaftar jiki.
Hukumar Lafiya ta Duniya (WHO) ta ce an samu fiye da mutum 61,000 da suka kamu da kwalara a yankin Afirka cikin watanni biyar na farkon shekarar 2026.
EU ta ce tallafin zai kuma taimaka wajen gano sababbin masu ɗauke da cutar cikin gaggawa, kula da marasa lafiya da kuma wayar da kan al’umma kan hanyoyin kare kai daga cutar.
Kwalara cuta ce da kwayar Vibrio cholerae ke haifarwa, kuma ta fi yaɗuwa ta hanyar shan ruwan da ya gurɓata.
Idan ta yi tsanani, tana iya jawo rashin ruwa mai yawa a jiki cikin ƙanƙanin lokaci.

