Home » Aƙalla Mutane 5 Sun Kamu da Cutar Kwarona – Hukumar NCDC

Aƙalla Mutane 5 Sun Kamu da Cutar Kwarona – Hukumar NCDC

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Hukumar yaki da cutuka masu yaduwa ta NCDC ta sanar da samun akalla mutane 5 da suka harbu da cutar corona a sassan kasar nan daga ranar 25 ga watan Fabarairu zuwa 31 ga watan Maris din da ya gabata.

Alkaluman da hukumar ta fitar a yau asabar sun nuna cewa sabbin kamuwa da cutar sun fito ne daga jihohin Lagos da Rivers wadanda kuma tuni aka killace su don dakile yaduwar cutar.

NCDC ta bayyana cewa mutum 4 suka harbu da cutar a jihar Lagos yayinda wani 1 ya harbu da ita a Rivers, lamarin da ke sanya fargabar yiwuwar dawowa da kuma YADUWAR cutar a sassan Najeriya.

Zuwa yanzu alkaluman NCDC na nuna cewa mutum dubu 266 da 665 suka harbu da cutar Covid-19 a Najeriyar tun daga lokacin da aka samu bullar cutar zuwa yanzu.

 NCDC tace a cikin jumullar wadanda suka kamu da cutar covid-19 a kasar nan mutum Dubu 259 da 951 sun samu warkewa yayinda cutar ta kashe mutum dubu 3 da 155 a jihohin kasar 36 da birnin Abuja.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?