• Home  
  • A kwai yuwuwar jihohi 14 da yankuna 31 su fuskanci ambaliyar ruwa ~ NEMA
- Labarai

A kwai yuwuwar jihohi 14 da yankuna 31 su fuskanci ambaliyar ruwa ~ NEMA

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta zayyana jihohi 14 da yankuna 31 da ka iya fuskantar mamakon ruwan sama mai karfin gaske wanda zai iya haifar da ambaliyar ruwa daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Yuli.

A kwai yuwuwar jihohi 14 da yankuna 31 za su iya samun ambaliyar ruwa ~ NEMA

Hukumar Bayar da Agajin Gaggawa ta Kasa (NEMA) ta zayyana jihohi 14 da yankuna 31 da ka iya fuskantar mamakon ruwan sama mai karfin gaske wanda zai iya haifar da ambaliyar ruwa daga ranar 4 zuwa 8 ga watan Yuli.

Hakan na kunshe ne cikin wata sanarwa mai dauke da sa hannun Mista Ibrahim Farinloye, Kodinetan NEMA, ya fitar.

Farinloye ya bukaci masu ruwa da tsaki a jihohin da abin ya shafa da su dauki matakan kariya domin dakile asarar rayuka da dukiyoyi.

Jihohin da yankunan da abin ka iya shafa su ne kamar haka:

Filato: Langtang da Shendam

Kano: Sumaila da Tudun Wada

Sakkwato: Shagari, Goronyo da Silame

Delta: a garin Okwe

Kaduna: a garin Kachia

Akwa Ibom: a Upenekang

Adamawa: a garuruwan Mubi, Demsa, Song, Mayo-belwa, Jimeta da Yola

Katsina: birnin Katsina, Jibia, Kaita da Bindawa

Kebbi: Wara, Yelwa da Gwandu

Zamfara: Shinkafi da Gummi

Borno: Briyel

Jigawa: Gwaram

Kwara: Jebba

Neja: Mashegu da Kontagora

Farinloye ya gode wa Hukumar Hasashen Ruwan Sama (FEWS) da Ma’aikatar Muhalli ta Tarayya Abuja bisa bayar da bayanan daminar bana a kan lokaci.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai