Home » Abin Da Yasa Aka Ɗage “Quran Convention” A Najeriya 

Abin Da Yasa Aka Ɗage “Quran Convention” A Najeriya 

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment

Majalisar Ƙoli Ta Addinin Musulunci A Najeriya ta ɗage taron mahaddata Al-Qur’ani da ake yi wa laƙabi da Qur’anic Convention a Turance da za a gudanar a Abuja Saboda yawan waɗan da suka nuna sha’awar zuwa. 

Bayanin ɗage taron na ƙunshe a cikin wata sanarwa da majalisar ta fitar a yammacin ranar Asabar 15 ga Fabarairun 2025.

Sanarwar ta ce, kwamitin shirya taron ya tsara karɓar mahaddata dubu 30 ne, amma yanzu haka sama da mutane dubu ɗari biyar sun bayyana sha’awar halartar taron.

A takardar sanarwar ɗage taron, an bayyana cewa, an samu dubban mutane daga ƙasashen ƙetare da suka bayyana sha’awar halartar taron, abin da ya wajabta wa majalisar neman kwamitin ya ɗage taron.

Majalisar ta nemi kwamitin shirya taron mahaddata Al-Qur’anin ya sake shiri na musamman domin karɓar masu niyyar zuwa taron.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?