Allah Ya Yi Wa Matar Tsohon Gwamnan Kano, Audu Bako, Rasuwa

Hajiya Ladi Audu Bako, wacce mata ce ga gwamnan Kano na farko a mulkin soji (1967 zuwa 1975), kwamishinan yan sanda Marigayi Alhaji Audu Bako, ta rasu tana da shekaru 93 a Duniya, bayan rashin lafiya ta tayi wacce har ta kai ga an kwantar da ita a Asibiti.

Za’ayi jana’izar ta da misalin karfe 2:00pm na rana a wannan Rana ta Laraba (5/4/2023) a fadar masarautar Kano, kamar yadda diyar ta, Zainab Audu Bako, ta bayyana.

Post masu alaƙa

Dan KAROTA da direba ya buge ya gudu Nasiru Abdullahi Mai Jihadi ya rasu ya bar mata 2 da ‘ya’ya 12.

An kama budurwa ‘yar shekara 15 kan safarar miyagun kwayoyi a Delta.

Uwargidan shugaban Najeriya Sanata Oluremi Tinubu ta kaddamar da rumbum abinci ga jama’ar kudu maso kudancin Najeriya.