Allah Ya Yi Wa Matar Tsohon Gwamnan Kano, Audu Bako, Rasuwa

Hajiya Ladi Audu Bako, wacce mata ce ga gwamnan Kano na farko a mulkin soji (1967 zuwa 1975), kwamishinan yan sanda Marigayi Alhaji Audu Bako, ta rasu tana da shekaru 93 a Duniya, bayan rashin lafiya ta tayi wacce har ta kai ga an kwantar da ita a Asibiti.

Za’ayi jana’izar ta da misalin karfe 2:00pm na rana a wannan Rana ta Laraba (5/4/2023) a fadar masarautar Kano, kamar yadda diyar ta, Zainab Audu Bako, ta bayyana.

Post masu alaƙa

Kotun kolin Najeriya ta tabbatar da hukuncin kwace kadarorin Godwin Emefiele

Dalibai huɗu za su wakilci Najeriya a gasar Spelling Bee ta Duniya a China

Babandede Ya Taya Shettima Murnar Sake Samun Takarar Mataimakin Shugaban Kasa