• Home  
  • Al’umma sun rabauta da tallafin Saudiyya a Kano
- Labarai

Al’umma sun rabauta da tallafin Saudiyya a Kano

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA), a ranar Talata, ta fara rabon kayan abinci da cibiyar agajin jin kai ta Sarki Salman ta bayar ga iyalai dubu 2,056 a nan jihar Kano. Cibiyar Sarki Salman na bayar da agajin jin kai ne ga mabukata a ƙasashe daban-daban a faɗin duniya. Shugabar hukumar NEMA, […]

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEMA), a ranar Talata, ta fara rabon kayan abinci da cibiyar agajin jin kai ta Sarki Salman ta bayar ga iyalai dubu 2,056 a nan jihar Kano.

Cibiyar Sarki Salman na bayar da agajin jin kai ne ga mabukata a ƙasashe daban-daban a faɗin duniya.

Shugabar hukumar NEMA, Hajiya Zubaida Umar, a lokacin da take kaddamar da rabon kayayyakin, ta ce, an yi hakan ne domin tallafa wa marasa karfi, da kuma dakile tsadar rayuwa.

Game Da Mu

Gidan Radio da talabijin mai kawo muku labarai akan rukunoni daban daban. Da Hausa Muke Magana.

Yi Mana Imel: info@muhasatvr.ng

Tuntuɓi: +(234) 912 222 1000

Manyan Labarai