Home » Amfani da karfin soja ba zai kawo karshen ‘yan bindiga ba ~ Kashim Shettima

Amfani da karfin soja ba zai kawo karshen ‘yan bindiga ba ~ Kashim Shettima

by Muhammad Auwal Suleiman
0 comment
Amfani da karfin soja ba zai kawo karshen 'yan bindiga ba ~ Kashim Shettima

Mataimakin shugaban Nijeriya Kashim Shettima ya ce amfani da karfin soji kadai ba zai magance matsalar ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane ba

Ya bayyana haka ne ranar Lahadi yayin wata ziyarar ta’aziyya da ya kai jihar Kano da ke arewacin kasar.

Yankin na Arewa maso Yammacin Nijeriya ya dade yana fama da matsalar hare-haren ‘yan bindiga da masu garkuwa da mutane, wadanda kan bi mutane har gida ko su tare kan hanya, ko kuma su je makarantu su sace dalibai.

Gwamnatin kasar ta dauki matakai daban-daban domin magance matsalar, ciki har da yin ruwan bama-bamai da jiragen sojin sama kan maboyar ‘yan bindigar.

Sai dai duk da wadannan matakai, matsalar na ci gaba da ta’azzara musamman a jihohin Zamfara da Kaduna, inda ‘yan bindiga suka hana mutane sukuni.

You may also like

Leave a Comment

Muhasa TVR kafa ce ta labarai mai cikakkiyar rajista wadda manufarta ita ce ilimantarwa, da wayar da kai da Inganta al’adun Hausawa da kuma nishaɗantarwa.
Muna nan a kan titin Guda Abdullahi gida mai lamba 19 a Farm Centre, jihar Kano.

Ra'ayi

Labarai da Dumi-dumi

©MuhasaTVR 2023. Ku nemi izini kafin yin amfani da duk abin da aka wallafa a wannan shafi

Are you sure want to unlock this post?
Unlock left : 0
Are you sure want to cancel subscription?