An cire Najeriya Daga Jerin Kasashe Na FATF Masu Halasta Kuɗin Haram

An cire Najeriya da Afirka ta Kudu daga jerin kasashen da aka fi saka wa ido saboda yawan aikata zamba da kuma halasta kuɗaɗen haram a duniya.

Ƙungiyar kula da irin waɗannan laifuka ta Financial Action Task Force (FATF) mai hedikwata a Faransa ta bayar da sanarwar cire ƙasashen biyu mafiya girman tattalin arziki a Afirka yau Juma’a bayan taronta.

Ta kuma cire ƙasashen Burkina Faso da Mozambique daga jerin nata na ƙasashen da take bayar da shawarar tsaurara saka ido a kan su saboda ayyukan masu damfara da halasta kuɗin haram.

A shekarar 2023 ne aka saka Najeriya da Afika ta Kudu ciki jerin, kuma FATF ta ce Najeriya ta ƙarfafa wa hukumomi gwiwar yin aiki tare.

Wata sanarwa daga fadar shugaban Najeriya ta ce Shugaban Ƙasa Bola Tinubu ya bayyana matakin a matsayin “gagarumin cigaba a yunƙurin Najeriya na gyaran tattalin arziki da kuma inganta ayyukan ma’aikatun gwamnati”.

Post masu alaƙa

Tinubu ya sanya hannu kan kasafin kuɗin 2026 na naira tiriliyan 68

Ƙungiyar muhaɗu mugyara ta bayyana Muhasa TVR a matsayin kan gaba wajen gyaran tarbiyyar al’umma.

Fursuna ya tsere bayan hatsarin motar jami’ai a Yobe