An fara caccakar sabbin ministocin tsaro daga Arewa

A wani labarin kuma sababbin ministocin tsaro, Muhammad Badaru Abubakar da Bello Matawalle, suna shan suka da caccaka daga ƴan Najeriya saboda rashin gogewar aiki a ɓangaren da aka ba su.

Masu sharhi kan al’amuran yau da kullum  sun ce naɗa su a matsayin manyan masu jagorantar harkar tsaro a Najeriya, na cikin abubuwa mafiya ba-zata da ban mamaki da shugaba Bola Ahmed Tinubu ya yi.

Babban ministan tsaron, Muhammad Badaru Abubakar, ya buɗi ido ne a fagen kasuwanci da masana’antu, kafin ya faɗa siyasa. Shi ma, BelloMatawalle bai sai komai kan harkar tsaro ba, tsohon malamin makaranta ne.

Post masu alaƙa

Jigawa Za Ta Bai Wa Alhazai Abinci Sau Uku a Rana a Hajjin 2026

Namadi Ya Kaddamar da Shirin Fadada Ilimi yayin da SLU ta Yaye Dalibai Sama da 4,000

Hukumar Jin Daɗin Alhazai Ta Jigawa Ta Taya Gwamna Namadi Da Musulmi Murnar Eid-el-Fitr