An Kama Yahaya Bello

Hukumar Yaƙi da Yi Wa Tattalin Arziƙi Zagon Ƙasa (EFCC), ta kama Tsohon Gwamnan Jihar Kogi, Yahaya Bello, kan zargin karkatar da kuɗaɗe a lokacin gwamnatinsa.

Jami’an EFCC sun bayyana cewa suna  yi masa tambayoyi dangane da zarge-zargen da ake masa.

Sai dai wasu rahotanni na cewa Yahaya Bello ya je ofishin EFCC ɗin ne da kansa ba kamo shi aka yi ba.

Idan ba a manta ba Yahaya Bello, ya shiga wasan ɓuya tsakaninsa da EFCC tun bayan da ya sauka daga mulki.

Duk da zarge-zargen da EFCC ke masa na karkatar da kuɗaɗe a lokacin da yake mulkin Jihar Kogi, Bello ya musanta aikata hakan.

Post masu alaƙa

Yar Najeriya ta kammala jami’ar Burtaniya da daraja ta daya (1st Class) a ilimin kimiyar samar da manhajar kasuwancin zamani.

Gwamnati ta buƙaci jama’a su guji taɓa kumfar da ta ɓulla a hanyar Kaduna-Abuja

A riƙa yi wa masu shirin aure gwajin miyagun ƙwayoyi :- Buba Marwa