An karya dokar ƙasa da ƙasa a Venezuela – MDD

Sakatare-Janar na Majalisar Ɗinkin Duniya, ya nuna damuwa cewa ba a mutunta dokokin ƙasa da ƙasa ba kan abin da Amurka ta aikata a Venezuela.

António Guterres ya bayyana haka ne a wani sako da aka karanta a taron gaggawa da majalisar ta kira kan batun na Venezuela.

“Abin damuwa ne matuka kan rashin mutunta dokar ƙasa da ƙasa a Venezuela.

“Lamarin zai iya janyo rashin daidaito a ƙasar, tasiri mara kyau a yankin da kuma yadda batun zai iya sauya yanayin dangantaka tsakanin ƙasashe,” in ji Guterres.

Post masu alaƙa

Kano: Gini Ya Rufta Kan Mutane 16 Ciki Har Da Yara Shida

KACRAN: Babu wani babban rikicin manoma da makiyaya a Yobe

CP Ibrahim Bakori ya kai gaisuwar ban-girma ga Sarkin Karaye tare da halartar bikin rantsar da yan NYSC.