An Sace Amarya A Sakkwato

Wasu ’Yan Bindiga dauke da muggan makamai sun sace wata amarya da ƙwayenta huɗu a Ƙaramar Hukumar Sabon Birni a Jihar Sakkwato ranar Asabar. 

‘Yan bindigar sun sace amaryar da kawayenta ne a garin Kwaren Gamba, da ke yankin Kuka Teke.

Rahotanni sun tabbatar da cewa wannan kauye na fama da hare-hare daga yaran kasurgumin dan ta’addan nan Bello Turji.

Wadan da suka shaida faruwar lamarin  sun ce ‘yan bindigar sun afka wa yankin sannan kuma tafi da waɗanda abin ya shafa, lamarin da ya jefa tsoro da tashin hankali a zukatan mazauna yankin.

 

Post masu alaƙa

Hukumar Road Safety Za Ta Ɗauki Tsattsauran Matakai Kan Masu Tuƙin Ganganci A Kano.

Ƴan sandan Kano sun ƙwato motocin sata 3 tare da kama mutane uku da ake zargi

Majalissar dinkin duniya ta ce miliyoyin mutane a Najeriya na iya fuskantar matsananciyar yunwa