Sojojin Najeriya sun ce aƙalla mutum shida da ake zargin mayaƙan Boko Haram tsagin ISWAP ne sun miƙa tare da iyalansu a jihar Borno da ke arewa maso gabashin ƙasar.
Mai magana da yawun rundunar Operation Hadin Kai Captain Mohammed Goni ne ya sanar da haka, inda ya ƙara da cewa binciken farko-farko ya nuna cewa mutanen sun fito ne daga maɓoyar mayaƙan da ke Guduf Bubayagwa da Chikide a tsaunukan Mandara duk a ƙaramar hukumar Gwoza.
Sojojin sun kuma ce sun ƙwato kimanin dalar Amurka 1,120, wayoyin salula biyu kirar Tecno, da wasu kayayyaki daban-daban.
Har ila yau, sojojin sun kama wani da ake zargi mai samar wa ISWAP da Boko Haram kayayyaki ne a shingen bincike na Molai a jihar, inda aka kama shi da magunguna.
Goni ya kuma ce dakarun da ke sansanin soji na Logomani a ƙaramar hukumar Ngala sun daƙile wani hari da aka kai a daren ranar 6 zuwa 7 ga Yuli, wanda ISWAP ta ɗauki alhaki.